Tsohon ɗan ƙwallon Mali Salif Keita ya rasu

top-news

Dan ƙwallon ƙafar da ya fara lashe kyautar gwarzon Afrika a 1970 - ɗan wasan Mali Salif Keita ya rasu.

Tsohon ɗan wasan ƙungiyar St Etienne ta Faransa ya rasu ne yana da shekara 76 a duniya.

Keita ya yi suna ne a ƙungiyar St Etienne, ta Faransa inda ya lashe kofuna uku a jere na lig din ƙasar.

NNPC Advert

Ya taimaka wa ƙasarsa zuwa wasan ƙarshe a gasar cin kofin Afirka a 1972.

Keita kuma ya taka leda ƙungiyoyi daban-daban a ƙasashen Faransa da Spain da Portugal